Kasuwanci

Koma bayan da kasuwancin duniya ya fuskanta sakamakon rikicin Gabas Ta Tsakiya

Informações:

Sinopsis

Shirin "Kasuwa Akai Miki Dole" tare da Ahmed Abba a wannan mako ya ɗora ne kan inda ya tsaya a makon jiya, game da gagarumin koma baya a fannin kasuwanci da tattalin arziki da duniya ke fuskanta masamman a bangaren makamashi, sakamakon yaƙin da kawancen Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran, da kuma martinin jamhuriyar musuluncin kan Isra’ila da muradun Amurka a kasashen labarawa suka janyo. A makon jiya, shirin ya tattauna wannan batu ne da malaman da muka gayyato, wato Dr. Aminu Idris Harbau masamanin tattalin arziki a tarayyar Najeriya, da Dr. Ibrahim Adamu na sashin nazarin yankin gabas ta Tsakiya a jami’ar Havard da ke Dubai na haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sai Mohammad Qaddam Sidiq Isa, mai sharhi kan al’amuran Yau da Kullum shima a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sai kuma Isma’il Albabawee ɗan jarida kuma ɗalibi a jami’ar Karbala a ƙasar Iraki. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.